Hanyar Koko zuwa Zuru a Kebbi: Matashi ya yi wa Gwamna Bagudu roko mai sosa zuciya

Wani matshi mai suna Yusuf Salisu Buzu, ya roki Gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu, domin ya gyara masu hanyar Koko zuwa Zuru, ita kuma Gwamnatin tarayya ta biya shi.



Salisu Buzu ya ce " Mai girma Gwamnan jihar Kebbi, ka taimaki al'umman Zuru, ka yi masu hanyar Koko zuwa Zuru, Gwamnatin tarayya ta biya ka. Kamar yadda ka saba faranta rayuwar al'ummaka".

"Mai girma gwamnan jahar kebbi Sen.Atiku Abubakar Bagudu (Matawallen Gwandu) ka taimaki al-ummar zuru ka faranta masu rayuwa kamar yadda ka saba faranta rayuwarka na jahar kebbi. 

Babu shakka al-ummar jahar Kebbi suna cikin al-ummar da suka more romon dimukradiyya, sakamakon irin yadda gwamnatin jahar Kebbi take kyautatama al-umma ta bangare daban daban, kama daga kiwon lafiya, ayukka, noma, samarda aiki ga al-umma da dai sauran abubuwan more rayuwa. 

Amma mai girma Gwamna kasan "Yan adam ajizai ne, duk da irin kokarin da kakeyi ba zamu barka hakanan ba, sai mun kara maka aiki duba da muna da tabbacin kai maijin kukan talakkawan ka ne. 

Mai girma gwamnan jahar kebbi ka taimaki al-ummar Zuru da hanyar Koko zuwa Zuru. Wallahi al-ummar Zuru suna cikin al-ummar da suka nuna soyayya gareka".

Daga Yusuf  Salisu Buzu


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt



Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN