Dattawan Arewacin Najeriya sun juya wa majalisar dokoki baya, duba dalili

Kungiyar dattawan arewacin Najeriya ta yi watsi da wata gayyata da wani kwamitin wucin gadi na majalisar dattawa ya yi wa jama'ar kasar domin su bayyana ra'ayinsu game da shirin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriyar. 


Kungyar ta Northern Elders Forum, wadda Farfesa Ango Abdullahi ke jagoranta, ta ce majalisar na so ne kawai ta bata lkacin 'yan kasar ba tare da ta aiwatar da abubuwan da suka kamata ba. 


Kungiyar dattawan arewar, wadda ta yi kira ga sauran kungiyoyin farar hula na yankin da su kauracewa gayyatar da majalisar dattawan ta yi, ta ce a ganinta duk wani shirin gyaran kundin tsarin mulki da za a yi bata lokaci da kudade ne kawai. 


Dokta Hakeem Baba-Ahmed, daraktan yada labarai na kungiyar ta Northern Elders Forum, ya yi wa AbdusSalam Ibrahim Ahmed karin bayani.

Source: BBC
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN