Kungiyar
dattawan arewacin Najeriya ta yi watsi da wata gayyata da wani kwamitin
wucin gadi na majalisar dattawa ya yi wa jama'ar kasar domin su bayyana
ra'ayinsu game da shirin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriyar.
Kungyar ta Northern Elders Forum, wadda Farfesa Ango Abdullahi ke
jagoranta, ta ce majalisar na so ne kawai ta bata lkacin 'yan kasar ba
tare da ta aiwatar da abubuwan da suka kamata ba.
Kungiyar dattawan arewar, wadda ta yi kira ga sauran kungiyoyin farar
hula na yankin da su kauracewa gayyatar da majalisar dattawan ta yi, ta
ce a ganinta duk wani shirin gyaran kundin tsarin mulki da za a yi bata
lokaci da kudade ne kawai.
Dokta Hakeem Baba-Ahmed, daraktan yada labarai na kungiyar ta Northern
Elders Forum, ya yi wa AbdusSalam Ibrahim Ahmed karin bayani.
Source: BBC
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/