Yan sanda 30 Ke Gadin Ƙauyuka 100 A Katsina – Masari

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya koka kan yadda ‘yan sanda gudan 30 ke kula da kauyuka guda dari a jihar Katsina.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi lokcin bikin Sallah da sojojin sama suka shirya a jihar.
Ya ce hakan ya sa suke tunanin samar da ‘yan sandan yankuna wadanda za su taimaka wajen kawo tsaro a jihar. Inda ya kara da cewa, muddin ba a dauki wannan mataki ba to ko da sojoji sun yi maganin ‘yan Bindigar wasu ‘yan ta’addan kan iya sake bulla Wasu wuraren.
Ya baiwa mutanen kauyukan shawarar su daina baiwa masu laifin mafaka saboda a rika samu ana gamawa da su ba tare da an kashe wanda ba su ji ba, ba su gani ba.
Hukumar sojin ta sha alwashin samar da Jirgi marar matuki da zai yaki rashin tsaro a yankunan Katsinan da Arewa Maso Gabas.

Source: alummata


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN