Za mu kawo karshen boko haram kafin karshen wannan shekara>>> AVM Sadiq Abubakar

Shugaban sojojin saman Najeriya, AVM Sadiq Abubakar ya bada tabbacin cewa a wannan shekarar ko kumama kamin karshen ta zasu gama da mayakan Boko Haram.

Ya bayyana hakane a yayin da yake magana da sojojin dake yaki da Boko Haram din a Borno inda yace kamin karshen shekararnan ko kuma zuwa karshenta zasu gama da Boko Haram.Yace dan haka sojojin su mayar da hankali wajan cimma wannan Buri.

Yace shugaba Buhari ya basu taimako da goyon baya wanda su taba samu ba a baya.Yace hakanan hukumar sojojin zata ci gaba da baiwa sojojin duk kwarin gwiwar da ya kamata. Yace ya gamsu sosai da yanda sojojin suke aiki.Abubakar yace sun samu jiragen yaki 22 sannan kuma akwai 16 dake kan hanya.

Yace wadannan jirage sun taimaka matuka wajan nasarorin da suke samu inda yace idan suka ci gaba da haka nan bada jimawa ba zasu zama sojojin sama mafiya karfi a Africa.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN