‘Yan kwamitin sakai sunyi aika-aika a jihar Bauchi inda suka hallaka wani matashi har lahira

Wannan lamarin ya faru ne ranar lahadi a jihar Bauchi, a yankin Zango dake jihar inda wasu ‘yan kungiyar sakai da aka fi sani da ‘Yan kwamiti suka jikkata wani matashi mai shekaru 21 wanda hakan ya jawo sanadin mutuwarsa.

Matashin mai suna Abdussalam Ibarahim wanda dalubine dake matakin aji na 2 a jami’ar jihar Bauchi.

An rawaito cewa Mahaifiyar matashin Aisha Ibrahim, ta kai rahoto ga kungiyar ‘yan vigilante don yiwa dan nata horo, saboda zarginsa da take na satar mata turmin zani.

Wani makoci na kusa, mai suna  Ningi, ya shaida ce wa, Aisha ta zargi danta da satar turmin zani Wanda aka  kiyasta bai kai N3,000 ba.

Ya kara da cewa bayan da ta tuhume shi kuma Abdulsalam ya musanta wannan zargi, Aish ta gayyaci kungiyar ‘yan sakai wanda takai da sun jikkata shi har yayi sanadin mutuwarsa.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda na jihar, Ahmed Wakil, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce hakika wannan laifin kisan kaine suka aikata.

Ya  kuma tabbatar da kame mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin.

Manyan Wadanda ake zargin sun hada da Adamu Babayo; Sauran biyun da ake zargin su ne Sani Babayo da Abubakar.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN