Tsoho mai shekara 70 a Duniya ya sha dan karen duka a hannun fusatattun matasa a jihar Niger

Allah ya tona asirin wani tsoho mai shekara 70 a Duniya bayan ya yi ma wata karamar yarinya mai shekara 8 fyade har sau biyu a unguwar Chanchaga da ke birnin Minna na jihar Niger.

Wanda aka kama mai suna Muhammad Sani Umar (Tela) ana zargin ya yi wa yarinyar fyade har sau biyu kuma ya bata N80.

Sahara Reporters ta ruwaito cewa asiri ya tonu nebayan yarinyar ta kamu da rahin lafiya, bayan wani lokaci mahaifiyarta ta kula cewa wani abu yana faruwa da yarinyar, sakamakon haka ta tambayeta ita kuma yarinyar ta kai mahaifiyar wajen wannan tsoho kuma daga isar su shagonsa sai yarinyar ta nuna shi da hannunta.

Ganin yarinyar da mahaifiyarta ke da wuya, tsoho bai yi gardama ba sai ya fara bayar da hakuri yana cewa a rufa masa asiri zai dauki nauyin jinyar yarinyar.

Nan take mahaifiyar yarinyar ta fasa kuwa jama'a suka taru kuma aka yi wa tsoho dan karen duka kuma aka kai shi gidansu yarinya inda ya yi bayani, kuma aka kara lafta masa na jaki daga matasa majiya karfi.

Daga bisani an mika shi ga jami'an yansanda domin fuskantar tuhuma a gaban Kotu.

Mahaifiyar yarinyar ta roki mahukunta cewa a yi ma diyarta adalci a kan lamarin, domin wannan tsoho yana da daurin gindi a wajen manya a Chanchaga da jihar Niger.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Allah ya tona asirin tsoho mai shekara 70 bayan ya yi wa yar shekar 8 fyade a Chanchaga jihar Niger

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN