Ranar Alhamis za a gabatar da hawan Arfa A Saudiyya

Hukumomin Saudiya sun bayyana ranar Alhamis 30 ga watan Yuli a matsayin ranar hawa Arafa, sakamakon rashin ganin jinjirin watan Zul Hajji a yau Litinin, abin da ke nuna cewar gobe watan Zul Kida zai cika 30. 
Kotun Kolin Saudiya ta ce ranar Laraba mai zuwa za ta zama ranar 1 ga watan Zul Hijja saboda cikar watan Zul Kida, abin da ya sa za a hau Arafat ranar Alhamis 30 ga watan Yuli.
A karkashin wannan tsari, ranar Juma’a 31 ga watan Yuli ta kasance ranar babbar Sallah ko kuma Eid-el Adha. 
Kimanin mutane dubu 1 ake sa ran za su gudanar da aikin hajjin bana saboda annobar coronavirus wadda ta tilasta wa mahukuntan Saudiya daukar matakin rage yawan mahajjata daga sassan duniya.
Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN