Wani karamin soja da ake zargin ya na fama da ciwon matsananciyar damuwa (depression) ya budewa wani babban soja wuta a ranar Laraba. Babban sojan ya mutu nan take.
Jaridar The Nation ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a jihar Borno kuma har yanzu rundunar soji ba ta saki bayanan sojan da aka harbe ba.
Shi kansa sojan da ya yi kisan ba a bayyana sunansa ba bayan sanin cewa karamin soja ne da ke aiki da bataliya ta 202 a karkashin rundunar soji ta 21 da ke Bama a jihar Borno.
Kanal Sagir Musa, mukaddashin jami'in hulda da jama'a na rundunar soji, ya ce; "wani karamin soji da ke tare da bataliya ta 202 a runduna ta 21 da ke Bama a jihar Borno ya tubure da misalin da 10:30 na ranar 29 ga watan Yuli, 2020, tare da budewa babban soja wuta, lamarin da ya zama silar mutuwarsa.
"Ya bude ma sa wuta ne a lokacin da ya zo wurinsa shi kuma ya na magana a waya. An kama karamin sojan tare da fara gudanar da bincike. Yanzu al'amura sun koma daidai."
Source: Legit
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/