Yanzu-Yanzu: Buhari ya bude tafiye-tafiye tsakanin jihohi

Gwamnatin Tarayya ta bude tafiye-tafiye tsakanin dukkan jihohi a fadin Najeriya.

Hakan na zuwa ne a ranar Litinin da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya karbi rahoto na biyar daga kwamitinsa na kar-ta-kwana kan yaki da cutar coronavirus, kan halin da ake ciki game da cutar a kasar.

“Ina farin cikin shaida muku cewa Shugaban Kasa… ba amince, sai dai ‘yan sauye-sauyen da za a sanar a nan gaba.

Sai dai ya ce tafiye-tafiyen za su fara ne daga ranar 1 ga watan Yuli, tsakanin karfe 5 na Asuba zuwa 10 na dare da a baya aka kebance manyan motoci masu dakon kayan abinci da kayan gwari da shi.

Za a bude makarantu

Boss Mustapha ya kara da cewa Shugaba Buhari ya amince a bude makarantu ga daliban ‘yan aji shida na firamare, da kuma ‘yan aji uku na karamar sakandare da kuma ‘yan aji uku na babban sakandare da ke shirin jarabawar kammala karatu.

Sai dai ya kara da cewa nan gaba za a sanar da matakan da za a bi wajen bude makarantun.

Ya kuma ce gwamantin ta amince da bude filayen jirgin sama cikin matakan kariyar cutar coronavirus.
Jawabin Boss Mustapha ya ce sassaucin na makonni hudu bai hada da sauran tarukan jama’a a.

Aminiya


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN