Tsawa ta kashe masu garkuwa da mutane su 18 yayin da suke tsakar raba kudin fansa

Tsawa ta kashe wasu mutum 18 da ake zargin cewa masu garkuwa da mutane ne a jihar Adamawa.

Wata majiya ta ce lamarin ya faru ne a karamar hukumar Toungo da ke jihar ta Adamawa.

Karamar hukumar Toungo tana kudancin jihar Adamawa, kuma ta yi iyaka da kasar Cameroun.

Rahotanni sun nu8na cewa  masu garkuwa da mutane suna tsakar raba kudin fansa na kusan naira miliyan ashirin N20m da suka karba daga wani attajiri, sai tsawa ta fada masu suka mutu nan take a wani daji.

Kakakin rundunar yansandan jihar Adamawa DSP Suleiman Nguroje ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ce lamarin ya faru ne a yankin kasar Cameroun da ke iyaka da karamar hukumar Tougo a jihar Adamawa da ke Najeriya.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN