Najeriya ta fita ajin kasashen da ke dauke da Polio

An dai share shekaru kusan 25 ana kai kawo da nufin tinkarar  shan Inna da ta yi nasarar nakasa daruruwan yara a cikin tarrayar Najeriya ta kuma halaka da daman gaske. Sai dai an yi nasarar kai karshen annobar tare da amincewar Hukumar Lafiya ta Duniya WHO a kan bukatar tarrayar Najeriyar na zare ta cikin kungiya ta kasashen da ke dauke da cutar a cikinsu.

Wannan bukata dai Hukumar Lafiya ta Duniya ta gabatar ga kwamitin da ke kula da yaki da cutar Polio a duniya, sannan ta samu amincewar 'yan kwamitin a wani abun da ke zaman matakin karshe a kan hanyar kare shan Inna. Najeriya ta share tsawon wattani har 45 ba tare da samun cutar Polio ba tun bayan irin ta ta karshe a Munguno a shekara ta 2017.

Dr Ehinare Osagie na zaman ministan lafiyar tarrayar Najeriya wanda ya ce sabon matakin na zaman na kan gaba a kokarin kai karshen cutar da a baya ta dauki hankali sakamako na adawa daga mafi yawan al'umma a kasar.

Ya ce “Mun cimma gaggarumin ci gaba, kuma ci gaban shi ne: yanzu mun zama kasar da Hukumar Lafiya ta Duniya  za ta ayyana a matsayin wadda ba ta da cutar shan'Inna cikinta. Wannan na da muhimmancin gaske domin kuwa mun dauki lokaci muna aiki tukuru domin kaiwa wannan matsayi, mun wuce shekaru uku da ake bukatar ganin ba'a samu cutar a kasarmu ba. Wannan yana nufin cewa mun fita a cikin ajin mara kyau na kasashen da ke dauke da cutar ta Polio. To sai dai kuma sai a watan Agusta ne muke shirin kawo wa shugaban kasar shaidar fitar da ke da tasirin gaske”

Tun daga shekarar 1996 ne Najeriyar ta fara yunkuri na kai karshen cutar kafin kuma malaman addini da ragowar al'umma a sashen arewacin kasar su nuna adawa bayan ayyanata a matsayin kokarin kaiyyade iyali a cikin yankin da ke zaman na kan gaba ga haihuwa a duniyar Allahu. Da kyar da gumin goshi ne dai sarakuna da hukumomi na kasar suka shawo kan al'umma tare da kyale komawa zuwa rigakafin Polio da ya yi nasarar kaiwa ya zuwa ci gaban da kasar ke takama da shi a halin yanzu.

A fadar Musbahu Lawal Didi da ke zaman shugaba na kungiyar masu dauke da cutar Shan Inna, akwai bukata ta ci gaba a cikin matakan kariya da kula da masu dauke da cutar a bangaren gwamnatin kasar. Cikin 'yan awoyin kalilan ne dai cutar ta Polio ke nakasa masu dauke da ita a yayin kuma da take halaka kusan kaso 10 cikin dari na yara 'yan kasa da shekaru biyar da cutar tafi yi wa Illa.

Rahtun DW-Hausa

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN