Mutum 6 sun mutu, gidaje 600 sun rushe bayan ruwan sama da iska mai Karfi a Kano

Dailytrust ta rawaito cewa mutum shida suka rasa rayukansu baya ga gidaje 600 da suka rushe sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da iska mai karfi a kananan hukumomi hudu a jihar Kano.

Kazalika wasu mutum 1,752 sun rasa muhallansu sakamakon iftila’in a cikin mako guda a jihar, inji Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano.

Shugaban hukumar Sani Jili ya ce wutar lantarki ta kashe daya daga cikin mamatan, sauran biyar din kuma gini ne ya fada a kansu.

Sani Jili ya ce iftila’in ya shafi Kananan Hukumomin Gwale, Gwarzo Rimin Gado, da kuma Kibiya ne a cikin a makon jiya.

Ya ce hukumarsa na jiran rahoton sauran kanana hukumomin da abin ya shafa yayin da ma’aikata ke kokarin tattara alkaluman barnar da aka samu.

A cewarsa Rimin Gado da Kibiya sun riga sun gabatar da rahotanninsu, har an tallafa musu da kayan rage radadi a matakin farko ga wadanda suka yi asara.

Kaya da aka rabawa mutanen kai tsaye sun hada da “kayan abinci, tufafi da kayan shinfida, sai kuma buhunan siminti”, inji shi.

Rahotun Jaridar Alummata

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN