Hukumar Civil Defence ta jihar Osun ta bayyana cewa ta samu korafi akan
wata mata data lalatawa mijinta Al’aura bisa zargin da take masa yana
cin amanarta.Me magana da ywun Hukukmar Civil Defence na jihar,
Daniel
Adigun ne ya bayyana haka inda yace wata mata, Omolara Seriki ce ta kai
musu korafin mijinta cewa baya kula da ‘ya’yansu hakanan baya bata
hakkinta a matsayin matarsa.Saidai da aka tuhumi mijin sai ya bayyana
cewa shekarar su 6 da aure amma matarnan baya hin dadin zama da ita duk
da suna da yara 2.
Yace ya gaji da cin zarafin da take masa shiyasa ya
bar mata gidan ya koma gefensa can da zama. Wata rana wata tazo kaimai
abinci sai ruwan sama ya fara, dan hakane ta tsaya ta fake.
Yace can
kawai sai yaji ana kwankwasa kofa, yana budewa sai yaga matarshi ce,
tana yin arba da wannan data kawo mai abinci sai fada ya kacame
tsakaninsu, nan ta kama mai maraina tana barazanar fizgesu, yace a nanne
sai ya suma.
Bai farka ba sai a gadon Asibiti inda aka mai aiki a
marainansa.Da aka tambayi matar tace kasheta yaso yayi shiyasa ta mai
haka. Ta kara da cewa ta dade tana zargin yana cin amanarta shine rannan
taje inda yake tare da wadda yake cin amanarta da ita ta kamashi.
Hutudole
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari