Kashe DPO da yansanda 7 a jihar Kogi, duba matakin gaggawa da IGP ya dauka kan yan fashi

Yansanda 8 tare da farar hula 1 sun mutu a garin Isunlu a jihar Kogi ranar Alhamis bayan wasu miyagun yan fashi da makami sun farmaki garin.

DPO na yansanda na cikin yansanda da yan fashin suka halaka bayan sun kai hari a ofishin yansandan, suka saki wadanda aka tsare, daga bisani suka harbe yansandan har lahira.

Rahotanni sun ce bayan yan fashin sun halaka yansandan, sai suka zarce zuwa wani Banki suka kwashi kudi da ba a san adadinsu ba.

Sakamakon haka shugaban yansandan Najeriya Muhammed Adamu ya bayar da umarnin kaddamar da gagarumin bincike domin kama yan fashin da suka yi wannan aika aika.

Hukumar yansandan Najeriya ta fitar da wannan sanarwa a shafinta na Twitter, cewa shugaban yansanda Muhammed Adamu ya abayar da umarnin yin binciken kwakwaf kan lamarin.

Tuni Shalkwatan yansandan Najeriya ta aika kwararrun jami'anta na sashen Intelligence Response Team (IRT), da Special Tactical Squad (STS) da Federal-SARS suna cikin wadanda IGP ya tura jihar Kogi domin su binciko, kuma su kamo wadanda suka aikata wannan danyen aiki ga jami'an yansanda.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN