Duba yara yan shekara 7 da 5 da mahaifinsu ya kashe ta hanyar duka da tabarya yayin da suke barci

Yansandan jihar Anambra sun kama wani mahaifi dan shekara 34 mai suna Ifeanyi Apusiobi daga garin Azu Ogbunike a karamar hukumar Oyi bayan ya kwantare diyansa biyu da tabarya har lahira.


Wannan mutum ya sami yayansa masu suna Chinecherem Apusiobi mai shekara 7 da kaninsa Obinna Apusiobi mai shekara 5 suna barci sai ya dinga dukansu da tabarya har suka mutu. 


Daga bisani kuma ya yi wa mahaifinsa mai shekara 72 manyan raunuka a kai.


Yansanda sun kai gawakin yaran Asibiti inda Likita ya tabbatar da mutuwarsu.


Yansandan sashen CID suna gudanar da binciken sirri kan lamari.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN