Daya da cikin yan bindiga da ke addabar jama'a a Shiroro ya fada hannu a jihar Niger

Yan sandan jihar Niger sun damke wani dan bindiga mai suna Ibrahim Muhammed.

Kakakin hukumar yansandan jihar Niger Wasiu Abiodun, ya ce yayin binciken ababen hawa na tsaya mu duba da yansanda suka yi a hanyar Minna zuwa Sarkin Pawa, yansanda sun tsayar da wani babur dauke da fasinja.

Bayan sun bincike kayan da aka dauko sai suka sami bindiga kiyar AK47 a wajen Muhammed wanda aka fi sani da suna Shagari Mayigyawa dan karamar hukumar Zaria a jihar Kaduna. Ganin haka sai mai babur ya gudu ya shige gandun daji.

Kakakin yansandan ya kara da cewa Muhammed na cikin yan bindiga da ke addabar bayin Allah a garin Sarkin Pawa da Shiroro.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN