Dokar taron ibada: Kotu ta ci tarar limaman Juma’a biyu a Bauchi, duba yawan kudin

Rahotun Jaridar Aminiya

Wata kotun tafi-da-gidanka a Bauchi ta yanke wa wasu limamai biyu hukuncin biyan tara ta N20,000 ko wanne, bayan ta same su da laifin jagorantar sallar Juma’a a masallatai daban-daban.

An gurfanar da limaman, Malam Musa Hassan da Malam Dahiru Alhaji, a gaban kotun ne ana tuhumar su da yin karan tsaye ga dokar gwamnatin jihar ta hana taruwa a wuraren ibada.

Duk su biyun dai a kauyen Dunkui Ambi na karamar hukumar Misau suke.

Kotun, a karkashin jagorancin Alkalin Majitare Muktar Abubakar, ta ce ba za ta yi wa duk wanda aka samu yana saba wa dokar jihar ta hana wasu harkoki da sauki ba.

Alkali Abubakar ya yi kira ga al’ummar jihar su yi biyayya ga umarnin hukumomi.

A yanzu haka dai gwamnatin jihar ta Bauchi ta haramta tarukan jama’a, ciki har da taruka a wuraren ibada, a yunkurin hana kwayar cutar coronavirus yaduwa.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN