Coronavirus: Gwamnati ta fara raba wa talakawa kudi kyauta

Rahotun Jaridar Aminiya

Gwamnatin Najeriya ta fara raba wa marasa galihu da ke Yankin Babban Birnin Tarayya N20,000 ko wanne don rage masu radadin dokar da aka ayyana ta hana fita a yankin.

Wadanda za su ci moriyar tallafin dai marasa galihu ne a yankin su 50,000 wadanda ke karkashin tsarin gwamnati na bayar da N5,000 duk wata bisa sharadi.

A jawabin da ya yi ranar Lahadi na ayyana dokar ta hana fita, Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya bayar da umarni a bai wa wadannan mutane kudin su har na watanni biyu nan take.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwato Ministar Ayyukan Jinkai da Agajin Gaggawa Hajiya Sadiya Umar yayin kaddamar da aikin a karamar hukumar Kwali tana cewa matakin bin umarnin shugaban kasa ne.

“Naira 5,000 ake bai wa masu cin gajiyar wannan tsari duk wata; don haka N20,000 din da za a bai wa ko wanne yanzu na wata hudu ke nan.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN