Yanzu-yanzu: Rikici ya barke a majalisar dokokin Kano kan tsige Sarki Sanusi

Rahotun Legit Hausa

Mambobin majalisar dokokin jihar Kano sun barke da fada da safen nan yayinda kwamitin binciken sarkin Kano, Muhammadu Sanusi na biyu, ke shirin gabatar da rahoton kwance masa rawani. Daily Nigerian ta ruwaito.

Rikicin ya fara ne yayinda mataimakin kakakin majalisar, Hamisu Chidari, ya nemi izinin gabatar da rahoton yau. Amma yan majalisar jam'iyyar adawa ta PDP suka ce a dakatad da gabatar da rahoton binciken sai ranar Talata domin kara dubi cikin rahoton; kawai sai rikici ya barke wanda ya kai ga dan majalisa mai wakiltar Warawa ya dauke sandar majalisa.

Masu idanuwan shaida sun bayyana cewa akwai alamun cewa yau za'a kwancewa sarki Sanusi rawani ko ta rahoton majalisar, ko kuma ta hukumar yaki da rashawar jihar.

Ku dakace cikakken rahoton...

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN