Yadda ’yan bindiga suka kashe mutum 51 a Kaduna

Rahotun Jaridar Aminiya

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai wani mummunan hari a kauyuka hudu da ke cikin Karamar Hukumar Igabi ta jihar Kaduna, inda suka kashe akalla mutum 51 yayin da suka raunata wasu da dama.

Kauyukan da aka kai harin sun hada da: Kerawa, Zareyawa da Marina duk a cikin garin Kerawa.
Maharan sun kai harin ne da misalin karfe 6:00 na safiyar ranar Lahadi, bayan jama’ar garin sun dawo sallar asubahi.

Aminiya ta samu rahoton cewa, an kone gidaje da dama sannan ‘yan bindigar suka kwashe kayan abincin mutanen da suka raunata.

Kansilan mazabar Kerawa, Malam Dayyabu Kerawa, ya tabbatar da aukuwar harin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar ASP Mohammed Jalige, ya ce  jami’an ‘yan sandan sun samu rahoton harin kuma sun tuntubi babban jami’in ofishin Karamar Hukumar don yin binciken.

ASP Mohammed, ya kara da cewa, da farko sun fara samun rahoton kashe mutum 37 a ranar Lahadi, amma daga bisani adadin ya karu.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika  
Saratu ta warke cutar olsa (ulcer) da ta yi fama da shi, karanta ababe da ta hada ta sha 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN