Wata matar aure ta kashe mijinta da wuka kan zargin yana lalata da wata a titi

Rahotun Legit Hausa

An tabbatar da mutuwar wani mutumi bayan matar shi ta caka masa wuka bayan wata rigima ta hada su a gidansu dake jihar Rivers yankin kudancin Najeriya Wani mai amfani da shafin kafar sadarwa na Facebook mai suna Anthony Biko Shadrach ya wallafa cewa matar dan uwanshi ta kashe shi da wuka saboda ta gano yana lalata da wata.

Ya ce: "Yanzu yanzu, duniyar nan ta zama abin tsoro, dan uwana ya rasa ransa sanadiyyar caka masa wuka da matarsa tayi. A wani martani da ya mayarwa da daya daga cikin abokanansa mai suna Kaandy, wanda yace ya jiyo maganganu da yawa akan wannan lamari na dan uwan nasa, Anthony ya kara da cewa:

 "Kawai wata 'yar karamar hatsaniya ce ta hado su da matarshi, koda ace yana zuwa yana lalata da wata ne ma bai kamata ta dauki rayuwarshi ba. Ana ta samun matsaloli tsakanin mata da miji a Najeriya dake kai ga daya ya dauki makami ya kashe daya duk kuwa da cewa kotu na hukunci akan duk wanda aka kama da hannu a irin wannan ta'asa.

A kwanakin baya dai babbar kotun Abuja ta yanke hukunci akan Maryam Sanda, matar da ta kashe mijinta akan zargin yana da wata budurwar a titi. Wannan hukunci na ta ya tada hankalin mutane da yawa a Najeriya musamman mata, sannan kuma ya jawo kace nace matuka a kasar ta Najeriya.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN