Coronavirus: An rufe makarantu a jihar Kebbi, duba dalili

An rufe makarantun framare da na gaba da faramare a jihar Kebbi , ciki har da makarantu masu zaman kansu na faramare da sakandare sakamakon umarni da gwamnatin jihar Kebbi ta bayar na rufe makarantun saboda barazanar cutar Coronavirus har tsawon kwana talatin.

Tun ranar Asabar aka sallami dalibai na makarantun kwana a jihar Kebbi, yayin da ranar Litinin 23/3/2020 aka sallami yan makaranta na jeka ka dawo.

Mujallar ISYAKU.COM ya samo cewa da safiyar Litinin, aka sallami yan makarantar sakandaren jeka ka dawo na mata zalla Salamatu Hussaini Girls Government Secondary School da ke unguwar Badariya a garin Birnin kebbi.

Haka zalika, mun samo cewa babu dalibi ko daya a makarantar kwana na yara maza zalla na kwalejin Nagari College da ke Makerar Gandu a Birnin kebbi.

Hatta makarantu masu zaman kansu, kamar Unique Progressive Primary and Secondary School da ke bayan babban filin wasa na Haliru Abdu da ke garin Birnin kebbi, sun rufe makarantar sakamakon biyayya ga umarnin gwamnatin jiha.


Tuni dai yara suka fara amfani da wannan dama domin yin wasa a unguwanninsu, lamari da ke haddasa cudani a tsakaninsu, marmakin su kasance a gidajensu wanda shi ne dalili da ya sa gwamnati ta bayar da wannan hutu.

Rahotun Isyaku Garba Zuru

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN