Rahotun Legit Hausa
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin bada gudunmuwar milyan hamsin cikin kudin tallafin da ake shirin baiwa yan Najeriya domin saukake radadin zaman gida sakamakon cutar Coronavirus.
Ya bayyana hakan ne a jawabin da ya saki ranar Laraba. Ya ce zai bada gudunmuwar ne ta kamfaninsa Priam Group inda har gwamnatin tarayya ta shirya samar da tallafi ga yan Najeriya.
Yace: “Ina jinjinawa dukkan mutane da kamfanonin da suka taimakawa yan Najeriya yayin wannan annoba. Ina kara kira ga wasu kamfanonin da masu hannu da shuni su taimakawa mutane a irin wannan lokaci.“
“Priam Group ta yi alkawarin N50 million a madadina matsayin gudunmuwar tallafin da ya za a yiwa yan Najeriya.“ Za ku tuna cewa daya daga cikin yaran Atiku Abubakar ya kamu da cutar kuma ana jinyarsa a asibitin koyarwan jamiar Abuja dake Gwagwalada.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya
Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari