Atiku ya yi alkawarin bada gudunmuwar N50m domin matsayin tallafi ga yan Najeriya

Rahotun Legit Hausa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin bada gudunmuwar milyan hamsin cikin kudin tallafin da ake shirin baiwa yan Najeriya domin saukake radadin zaman gida sakamakon cutar Coronavirus.

Ya bayyana hakan ne a jawabin da ya saki ranar Laraba. Ya ce zai bada gudunmuwar ne ta kamfaninsa Priam Group inda har gwamnatin tarayya ta shirya samar da tallafi ga yan Najeriya.

Yace: “Ina jinjinawa dukkan mutane da kamfanonin da suka taimakawa yan Najeriya yayin wannan annoba. Ina kara kira ga wasu kamfanonin da masu hannu da shuni su taimakawa mutane a irin wannan lokaci.“

“Priam Group ta yi alkawarin N50 million a madadina matsayin gudunmuwar tallafin da ya za a yiwa yan Najeriya.“ Za ku tuna cewa daya daga cikin yaran Atiku Abubakar ya kamu da cutar kuma ana jinyarsa a asibitin koyarwan jamiar Abuja dake Gwagwalada.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN