2023: Kungiya ta shirya tsaf domin mara wa Abubakar Malami a Birnin kebbi

Wata kungiya mai karadin ganin Ministan shari'a na Najeriya Abubakar Malami SAN ya fito takaran Gwamnan jihar Kebbi mai suna Khadi Malami Progressive Association, ta gudanar da tatattaunawa a garin Birnin kebbi.

Yan kungiyar sun hadu a kofar gidan Sarkin Fawa da ke unguwar tsohuwar kasuwa ranar Asabar 21/3/2020 inda suka tattauna kan alfahari da yiwuwar fitowar dan unguwar Junju, domin takarar kujerar Gwamnan jihar Kebbi a 2023.

Haka zalika, yan kungiyar, sun tattauna yadda za su shiga Birni da kauyuka domin nemo jama'a su mara wa tafiyar.

Daga karshe, 'yan kungiyar sun sha alwashin cewa za su shiga yin kamfen, domin wannan tafiya idan lokaci ya yi, kuma a yanzu, sun dukufa ne domin bayyana ayyukan alkhairi da Abubakar Malami yake yi wa jama'a.

Zaman ya sami jagorancin shugaban kungiyar Dan Yaya Milo, tare da Sakataren kungiyar Ahmed Didiyu. Sai kuma Dattijan kungiyar Mal.Habibu B, Bashir Magini da Mansur S. Fawa.

Kungiyar na da tsari gida uku da suka hada da manyan matasa, kananan matasa da kuma mata.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN