Zargin barazanar sauke shugabannin kananan hukumomin APC na jihar Zamfara

Wasu bayanan sirri da suka bayyana sun zayyana zargi da ake yiwa Gwamnan Jihar Zamfara Bello Matawalle da yin barazana ga Shuwagabannin kananan hukumomin guda 14 na jam'iyar APC kan sauke kowane daga cikin su wanda bai sauya sheka zuwa jam'iyar gwamna ta PDP ba.

Wannan zargi da ake yiwa Gwamna  Matawalle ya tafi akan cewar Gwamna Matawalle ya yi dukkan barazana akan shuwagabannin kananan hukumomin na jihar zamfara wanda duk suke biyayya ga jam'iyar APC da cewar, duk wanda be aminta da sauya sheka zuwa jam'iyar PDP ba akwai shirin dauko masa lamarin shari'un zaben da kuma gabatardashi a gaban yan majalisar dokokin na jihar zamfara don amsa tambayoyi.

Hakazalika, bayanin na zargi da ake yiwa Gwamna Matawalle, ya nuna cewa Gwamna Matawalle ya sha alwashin kyale duk wani Shugaban karamar hukuma wanda ya canja sheka zuwa PDP a saman kujerar sa ta Shugaban karamar hukuma.

"Yana da kyau dai mu tuna cewar wadannan shuwagabannin kananan hukumomi 14 na jam'iyar APC an zabe su ne akan dokar zabe ta kasa, da kuma dukkan dokokin da akebi wajen zaben kowane shugaba na karamar hukuma don haka zargin yunkurin sauke su da Gwamna Matawalle yake ba adalci ba ne kuma saba dokar kasa ne" inji wani Musa Gusau..

Matasa Masu Kishin Jihar Zamfara.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN