Rahotu Legit Hausa
Wani mutum a kasar Brazil ya amsa cewa ya kashe matarsa ne a
yayin da suke tsakiyar saduwa saboda fushin cewa ta sake samun juna biyu karo
na uku.
Marcelo Araujo dan shekara 21 ya shaidawa 'yan sanda a Sao
Paulo bayan an shafe makonni shida ana masa tambayoyi cewa ya kashe matarsa mai
sana'ar yi wa mutane kwaliya, Francine dos Santos, mai shekaru 22 bayan sunyi
musayar kalamai kan juna biyun da ta sake dauka karo na uku.
Ya bayyana cewa baya son karin haihuwa saboda ya ki jinin
yadda hankalin matar ke rabuwa tsakaninsa da yaran kuma yana matukar damuwa
saboda kudin da ya ke kashewa domin kulawa da yaran. Ma'uaratan suna da yara
biyu, mace mai shekaru hudu da na miji dan shekara biyu.
Da ya ke bayar da ba'asi kan yadda rikicinsu ya samo asali,
Mista Araujo ya yi ikirarin cewa a watan Decemban 2019, sun fara tattauna yadda
za su yi bikin Kirsimeti amma sai suka fara musayar kalamai a kan juna biyun da
ta ke dauke da shi.
Jim kadan bayan sun kammala musayar kalaman, sun huce
fushinsu kuma suka nufi daki domin suyi kwanciya irin ta masoya. A yayin da
suke tsakiyar saduwa ne wanda ake zargin ya yi amfani da wuka ya yi ta caka wa
matarsa kuma daga bisani ya yanke ta a wuya.
Bayan ya aikata laifin, ya yi yunkurin ya kashe kansa. Yan
sanda sun tsinci shi da munanan rauni a wuyansa da hannunsa a gidansu da ke
Varzea Paulista da ke jihar Sao Paulo.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari