Gwamnatin jihar Kano ta rufe kamfanin Sani Danja

Rahotun BBC Hausa

Fitaccen tauraron fina-finan Kannywood, Sani Danja, ya yi zargin cewa hukumar tace fina-finan jihar Kano ta rufe kamfanin daukar hotonsa saboda siyasa.

Sai dai hukumar ta ce ta dauki matakin ne saboda kamfanin bai cika sharudanta na yin rijista ba.
Tauraron ya shahara wajen goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da jam'iyyar PDP da ke hamayya a Kano, wanda ya raba gari da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje tun bayan zaben 2015.

A wata tattaunawa da ya yi da BBC, tauraron ya ce, "Babu wata maganar yin rijista, akwai da ma mutanen da ake hakonsu saboda dalilai na siyasa."

Sani Danja ya ce sai da ya yi rijista da dukkan hukumomin da ke kula da harkokin kasuwanci kafin ya bude kamfanin daukar hoton, ciki har da Hukumar rijstar harkokin kasuwanci ta Najeriya, Corporate Affairs Commissioin.

Sai dai shugaban hukumar tace fina-finai ta Kano, Malam Isma'ila Na'abba Afakallah ya shaida wa BBC cewa ba makarkashiyar siyasa ce ta sanya suka rufe kamfanin tauraron ba, yana mai cewa rashin yin rijista ne.

"Babu wani gida[na daukar hoto] da muka rufe don yana daukar hoto; mai yiwuwa idan gidan daukar hoton wanda kake magana a kai [Sani Danja] ya fado cikin wadanda basu yi rijista ba, to an rufe shi," in ji shi

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN