Rahotun BBC Hausa
Fitaccen
tauraron fina-finan Kannywood, Sani Danja, ya yi zargin cewa hukumar
tace fina-finan jihar Kano ta rufe kamfanin daukar hotonsa saboda
siyasa.
Sai dai hukumar ta ce ta dauki matakin ne saboda kamfanin bai cika sharudanta na yin rijista ba.
Tauraron ya shahara wajen goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Sanata
Rabi'u Musa Kwankwaso da jam'iyyar PDP da ke hamayya a Kano, wanda ya
raba gari da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje tun bayan zaben 2015.
A wata tattaunawa da ya yi da BBC, tauraron ya ce, "Babu wata maganar
yin rijista, akwai da ma mutanen da ake hakonsu saboda dalilai na
siyasa."
Sani Danja ya ce sai da ya yi rijista da dukkan hukumomin da ke kula da
harkokin kasuwanci kafin ya bude kamfanin daukar hoton, ciki har da
Hukumar rijstar harkokin kasuwanci ta Najeriya, Corporate Affairs
Commissioin.
Sai
dai shugaban hukumar tace fina-finai ta Kano, Malam Isma'ila Na'abba
Afakallah ya shaida wa BBC cewa ba makarkashiyar siyasa ce ta sanya suka
rufe kamfanin tauraron ba, yana mai cewa rashin yin rijista ne.
"Babu wani gida[na daukar hoto] da muka rufe don yana daukar hoto; mai
yiwuwa idan gidan daukar hoton wanda kake magana a kai [Sani Danja] ya
fado cikin wadanda basu yi rijista ba, to an rufe shi," in ji shi
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari