Jam'iyar APC a jihar Zamfara ta yi asarar kimanin mambobinta guda 20,000 bayan sun canja sheka zuwa jam'iyar PDP.
Jaridar DailyPost ta ruwaito cewa wadanda suka canja shekan sun fito ne daga kananan hukumomin Bakura da Gummi.
Yayin da yake karbar wadaanda suka canja shekan a gidan Gwamnati da ke Gusau, Gwamna Bello
Mohammed Matawalle ya ce wannan babban asara ne ga jam'iyar APC a jihar.
Matawalle ya yi kira ga al'umman jihar Zamfara, su bayar da nasu gudunmuwa domin ci gaban jihar, ba tare da la'akari da banbancin siyasa ba.
Ya ce Gwamnatinsa ta dukufa wajen ganin ta samo kwararru da masana domin ganin cewa an ciyar da jihar gaba.
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari