An raunata mutum biyu bayan an caka masu wuka lokacin da fada ya kaure tsakanin Yarbawa da Hausawa a kasuwar Lafenwa da ke Abeokuta babban birnin jihar Ogun.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa kakakin hukumar yansandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin , ya ce babu asarar rai.
Punch ta ce, rigimar ya faru ne bayan wata jita-jita cewa wasu da ake zargin cewa matasan kabilar Yarbawa ne sun kashe wani Bahaushe.
Oyeyemi ya ce an kama mutum hudu, tare da wukake takwas, bayan mumunar tashin hankalin da ya gudana.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari