An tsinci gawar wani Almajiri da aka gundule kansa aka jefar da shi a kan titi a Beji da ke Minna a jihar Niger. Ba a san wadanda suka aikata wannan danyen aiki ba kawo yanzu.
Amma mazauna wannan unguwa sun yi zargin cewa matsafa ne suka gundule kan Almajirin, domin gudanar da lamarin tsafi.
Hakazalika jama'a na cikin fargaba, ganin yadda wannan lamari ya faru a unguwar. Sun yi kira ga hukumomi cewa su yi bincike kan lamarin domin ganin cewa hakan bata sake faruwa ba, tare da kama wadanda suka aikata wannan aiki.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari