Duba jarabawa da ya sa wani mutum ke neman taimakon gaggawa a Birnin kebbi

Sashen jakar Magori na Mujallar ISYAKU.COM, ya samo yadda iyalin wani bawan Allah ke neman fadawa cikin wani yanayi sakamakon yadda mai gidan mai suna Lawali Usman (Taloni) ya sami kanshi cikin jarabawan rashin lafiya mai tsanani.


Wakilin mu na garin Birnin kebbi ya samo cewa Lawali mazauni unguwar Haliru Abdu a garin Birnin kebbi, ya sha fama ta hanyar jeka ka dawo domin duba rashin lafiyarsa a Asibitin Sarki Sir Yahaya a Birnin kebbi, tare da taimako, agaji da tausayawa na makwabta da abokan arziki kan rashin lafiyarsa. Amma yanzu haka lamarin ci gaba yake yi, sakamakon haka Likitoci suka tura shi Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin kebbi domin ci gaba ada samun kulawa.,

Bincike da wakilinmu ya gudanar , ya nuna cewa yanzu haka, iyalin wannan bawan Allah na matukar neman agaji daga bayin Allah , sakamakon yadda gaba daya abin da iyalin suka mallaka ya tafi wajen neman magani., don haka suke neman jama'a su taimaka masu da abin da Allah ya hore.


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN