Sashen jakar Magori na Mujallar ISYAKU.COM, ya samo yadda iyalin wani bawan Allah ke neman fadawa cikin wani yanayi sakamakon yadda mai gidan mai suna Lawali Usman (Taloni) ya sami kanshi cikin jarabawan rashin lafiya mai tsanani.
Wakilin mu na garin Birnin kebbi ya samo cewa Lawali mazauni unguwar Haliru Abdu a garin Birnin kebbi, ya sha fama ta hanyar jeka ka dawo domin duba rashin lafiyarsa a Asibitin Sarki Sir Yahaya a Birnin kebbi, tare da taimako, agaji da tausayawa na makwabta da abokan arziki kan rashin lafiyarsa. Amma yanzu haka lamarin ci gaba yake yi, sakamakon haka Likitoci suka tura shi Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin kebbi domin ci gaba ada samun kulawa.,
Bincike da wakilinmu ya gudanar , ya nuna cewa yanzu haka, iyalin wannan bawan Allah na matukar neman agaji daga bayin Allah , sakamakon yadda gaba daya abin da iyalin suka mallaka ya tafi wajen neman magani., don haka suke neman jama'a su taimaka masu da abin da Allah ya hore.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari