Wata matar aure ta daba wa mijinta wuka a zuciya domin ya hanata yin yaji

Legit Hausa

Jami'an hukumar 'yan sandan kasar Kenya ta cafke wata mata mai suna
Mercy Wanjiru wacce ake zargi da soka wa mijinta mai suna Kevin Kuria
wuka a kirji saboda ya hana ta barin gidansu na aure da sunan yaji.
Lamarin ya faru ne ranar Alhamis, 12 ga watan Disamba, a yankin Nakuru
dake kasar Kenya yayin da Mercy ta kwashe kayanta domin barin gidan
mijinta bayan fada-fadacen da suka saba yi sun ki ci sun ki cinye wa.

Ganau ba jiyau ba sunce Mercy wacce ta soki mijinta a kirji ta ce ta
yi hakan ne domin kokarin kare kanta bayan da mijinta, Kelvin, ya nemi
sukarta da wuka. Daniel Thiongo ya ce: "An ga akwatinta dankam da kaya
amma mijinta ya hana ta tafiya, a lokacin da aka kirani don insa baki
domin sulhunta su.

Amma da na isa gidan sai naga Kelvin a kwance a
kasa, jini yana zuba daga kirjinsa." An kara gano cewa, wacce ake
zargi da kisan kan ta dinga kiran makwabta da abokai don neman
taimakon a kaishi asibiti.

An mika gawar mamacin zuwa asibitin Nakuru
don adana ta, yayin da ita kuma Mercy aka garkame ta a ofishin 'yan
sanda. Kwamandan ofishin 'yan sandan Nakuru, Stephen Matu ya ce: "A
halin yanzu, ana cigaba da bincike kuma za a mika wacce ake zargi
gaban kuliya a ranar Juma'a domin ta fuskanci tuhume - tumen da ake yi
mata.
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN