Shugaba Buhari ya bayar da umarnin a sake gaggauta daukan 'yan sanda 400,000

Legit Hausa

Ma'aikatar kula da harkokin da suka shafi rundunar 'yan sanda ta ce ta
samu umarnin gagga wa daga fadar shugaban kasa a kan ta dauki sabbin
'yan sanda 400,000 domin magance karancin da jami'an tsaro keda shi.

Da yake sanar da hakan ranar Litinin, shugaban sashen hulda da jama'a
na ma'aikatar, Odutayo Oluseyi, ya bayyana cewa tuni ministan
ma'aikatar kula da harkokin 'yan sanda ya kafa kwamitin mutane 13
domin fitar da tsarin yadda za a dauki karin sabbin jami'an.

Umarnin fadar shugaban kasar ya kawo karshen tababar da ake yi a tsakanin
hukumar kula da harkokin 'yan sanda (PSC) da kuma ofishin babban
sifeton rundunar 'yan sanda (IGP) a kan waye yake da alhakin daukan
sabbin jami'an 'yan sanda. Oluseye ya bayyana cewa kwamitin da
ministan ya kafa ya kunshi mambobi daga PSC da kuma rundunar 'yan
sanda.

Ya kara da cewa aikin kwamitin shine fito da tsarin da za a yi
amfani da shi wajen daukan sabbin jami'an bisa tsarin gwamnatin
shugaba Buhari na bawa tsaro fifiko. A cewar Oluseye tuni minista
Dingyadi ya rantsar da kwamitin tare da sanar da cewa daukan sabbin
jami'an na daga cikin shawarwarin da kwamitin mataimakin shugaban
kasa,

Farfesa Yemi Osinbajo, ya bayar a kan aiyukan da ya kamata
gwamnati ta bawa fifiko domin cimma manufofinta kamar yadda ta dauki
alkawari tun lokacin yakin neman zabe. Shugaba Buhari ne ya kafa
kwamiti a karkashin Osinbajo domin duba nasarorin da gwamnatinsu ta
samu da kuma haska mata bangarorin da ya kamata ta mayar da hankali a
zangonta na karshe, daga 2019 zuwa 2023.
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN