Mutumin da ya yi ta dukan matarsa har ta mutu ya shiga hannu

Wani magidanci mai shekara 37 da ya yi ta dukan matarsa har ta mutu ya shiga hannu a jihar Ogun.

A wata sanarwar da mai magana da yawun Rundunar ‘yan sandan jihar DSP Abimbola Oyeyemi, ya aikewa Aminiya ya shaida cewa jami’an rundunar sun kame Mutiu Sonola, wanda ake zargi da kashe matarsa Zainab Shotayo a jiya Laraba bayan da mahaifinta ya kai kararsa ga ‘yan sanda.

Ya ce, Mahaifin marigayiyar ya shaida cewa wanda ake zargin ya dade yana jibgar matarsa a duk lokacin da dan sabani ya shiga tsakanin su, ya ce ana ci gaba da bincike akan wanda ake zargin kana za a gabatar da shi a gaban kotu.

Hakki: Rahotun jaridar Aminiya

DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA Facebook.com/isyakulabari Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN