An kashe mutane 11 a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Rahotun TRT Hausa

Mutane 11 ne sula rasa rayukansu sakamakon rikicin da aka yi tsakanin 'yan kasuwa da wasu bata-gari a Banjui Babban Birnin Jamhuriyar Aflrka ta Tsakiya.

Labaran da jaridun kasar suka fitar sun ce an samu rikici tskanon 'yan kasuwa da 'yan tawaye kan biyan haraji a unguwar PK5 da mafiya mazaunanta Musulmi ne.

Sakamakon rikicin an kashe mutane 11 tare da jikkata wasu ds dama inda aka kuma kona shaguna da wuraren sana'a.

Duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanya hannu a kai a kasar a 2012 amma har yanzu an kasa zama lafiya a Banjui da wasu yankunan kasar.

A shekarar 2013 an gwabza rikici da ya koma yakin basasa tsakanin Kiristocin Anti-Balaka da Musulmi mafiya rinjaye Seleka inda aka kashe dubunnan mutane.

DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA Facebook.com/isyakulabari Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN