Legit Hausa
Yayin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tare a kasar
Ingila inda ya ke sararawa har zuwa Ranar 17 ga Watan Nuwamba, ya bar Najeriya
ba tare da ya mikawa mataimakinsa mulki ba.
Daga Birtaniya dai shugaban kasar ya sa a hannu a kan wani
kudiri da majalisa su ka amince da shi. Ganin haka ya sa aka dawo da korafin
cewa Abba Kyari ya na da ikon da ya zarce kima. Wannan mataki da shugaban kasar
ya dauka ya dade ya na jawo surutu da ce-ce-ku-ce.
Yanzu dai Daily Trust ta kawo jerin wasu ayyukan da Yemi
Osinbajo ya yi a lokacin da ya samu dama.
1.
EFCC: Ibrahim Magu Bayan wata tafiyar shugaban
kasar ne Mataimakinsa ya aika takarda ga majalisa domin ta tabbatar da Ibrahim
Magu a matsayin shugaban hukumar EFCC. A karshe Sanatoci ba su yi hakan ba.
2. CJN: Walter Samuel Onnoghen
A
farkon 2017 ne Farfesa Yemi Osinbajo ya aika sunan Walter Samuel Onnoghen gaban
majalisa domin a tabbatar da shi a matsayin Alkalin Alkalai. Bayan tabbatar da
shi, daga baya ya bar kujerarsa.
3. Tsige Lawal Daura daga DSS
Wani
babban matakin da Yemi Osinbajo ya dauka a lokacin da ya ke rike da Najeriya
shi ne sauke Mista Lawal Daura daga kujerar shugaban hukumar DSS bayan
jami’ansa sun zagaye majalisar tarayya.
4. SARS zuwa FSARS
Haka zalika
yayin da ya ke kan kujerar mukaddashin shugaban kasa, Osinbajo ya rusa hukumar
SARS inda ya maida ta FSARS bayan koke-koken dinbin jama’a game da zaluncin
jami’an tsaron a Najeriya. Ana rade-radin cewa wasu matakan da Osinbajo ya
dauka sun hada shi fada da na-kusa da Mai gidansa. Dama can ana zargin shugaban
ma’aikatan fadar shugaban kasan da rike madafan iko.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp