Melaye vs Adeyemi: APC ta yi wa PDP fintinkau a sakamakon kananan hukumomi 4 cikin 7

Legit Hausa

Smart Adeyemi, dan takarar jam'iyyar APC a zaben kujerar sanatar
mazabar Kogi ta yamma yana gaba da Dino Melaye na jam'iyyar PDP a
sakamakon kananan hukumomi hudu cikin bakwai da aka fitar kawo yanzu.
Yayin da Adeyemi ya samu kuri'u 5,609 a kananan hukumomi hudun, Melaye
ya na da kuri'u 1882 hakan na nuna akwai banbancin kuri'u 3,727
tsakaninsu.

A karamar hukumar Lokoja, Adeyemi ya samu kuri'u 4,659,
Dino kuma ya samu 920. A Mopa Morou, dan takarar na jam'iyyar APC ya
samu kuri'u 309 yayin da abokin karawarsa na PDP ya samu kuri'u tara
tak.

Duk da cewa Melaye ya samu rinjaye da kuri'u kalilan a Koton
Karfe da Ijumu inda 'yan takarar biyu suka fito, kayen da ya sha a
kananan hukumomi biyu sun yi masa illa a zaben. Melaye ya samu kuri'u
376 a karamar hukumar Koton Kafe yayin da Adeyemi ya samu kuri'u 287.
A Ijumu, dan takarar na PDP ya samu kuri'u 577 yayin da abokin
karawarsa na APC ya samu kuri'u 364.

A halin yanzu ana jiran sakamakon
sauran kananan hukumomin a lokacin hada wannan rahoton. Hukumar zabe
INEC ta bayyana zaben ranar 16 ga watan Nuwamba a matsayin wanda bai
kammalu ba wato (inconclusive) kasancewar kuri'un da aka soke sunfi
yawan wadanda wanda ke kan gaba ya bada tazara. Adeyemi ya samu jimla
kuri'u 80,118 yayin da Melaye ya samu kuri'u 59,548. Hakan na nuna
akwai tazarar 20,570 yayinda aka soke kuri'u 43,127.
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN