Legit Hausa
Za a gudanar da sabon zaben sanatan Kogi ta yammaa tsakanin
Sanata Dino Melaye na jam’iyyar PDP da Sanata Smart Adeyemi na jam’iyyar APC a
ranar 16 ga watan Nuwamba, kamar yadda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta
sanar.
Hukumar INEC a wani jawabi dauke das a hannun Mista Festus
Okoye, Shugaban kwamitin bayanai na hukumar, ya bayyana cewa za a hada zaben
sanatan ne tare da na gwamnan Kogi. Okoye, kwamishinan zabe na kasa, a wwani
jaabi da ya gabatar ga manema labarai a ranar Litinin a Abuja, ya bayyana cewa
za a kuma gudanar da zaben cike gurbi ga mazabar Sabuwa a jihar Katsina a ranar
30 ga watan Nuwwamba.
“Hukumar ta yanke shawarar ne a ganawar da tayi a ranar
Litinin,” cewar jawabin. Ya bayyana cewa sabon zaben ya biyo bayan soke zaben
sanata na Kogi ta Yamma da kotun zabe tayi sannan kotun daukaka karat a
tabbatar da hakan. Kotun daukaka kaa ta jaddada hukuncin kotun zabe wacce ta
soke zaben Dino Melaye na PDP, biyo bayan wata kara da Sanata Smart Adeyemi na
APC ya shigar.
Kotun daukaka karan,
a ranar 11 ga watan Oktoba ta umurci INEC da ta gudanar da sabon zabe cikin
kwwanaki 90 daga ranar da ta yanke hukunci . Okoye ya roki yan takarar da
jam’iyyun da su gudanar da kamfen daidai da tsari.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp