Ana saura wata daya
gudanar da zaben jihar, an tsige mataimakin gwamnan jihar Kogi, Simon
Achuba.
Majalisar dokokin jihar sun tsige Mista Achuba ne a Lokoja, babbar
birnin jihar, ranar Juma'a 18 ga Oktoba, 2019.
Shugaban masu rinjaye a majalisar ya bayyana hakan ne ga manema labarai a
zauren majalisar.
Legit.ng ta kawo muku rahoton cewa Wani kwamitin binciken a kan zargin
da ake yiwa mataimakin gwamnan Kogi Simon Achuba, wanda Barista John
Baiyeshea ke jagoranta ya mika rahotonsa zuwa ga Majalisar jihar.
Alkalin alkalan jihar Kogi, Jastis Nasir Ajanah shi ne ya kafa wannan
kwamitin. John kuma wanda shi ne shugaban kwamitin ya jagoranci mika
rahoton binciken zuwa ga Kakakin majalisar jihar a ranar Juma’a 18 ga
watan Oktoba, 2019.
Kakakin majalisar, Kolawole Matthew ne ya karbi rahaton daga hannun
shugaban kwamitin a Majalisar jihar dake Lokoja.
Da yake magana bayan mika rahoton shugaban kwamitin ya ce sun yi iya
bakin kokarinsu na yin bincike na gaskiya.
A cewar shugaban, John Baiyeshea, a shirye kwamitinsu yake domin amsa
duk wata tambaya da ta shafi abinda rahoton nasu ya kunsa. Kuma ya kara
da cewa rahoton ya kasu zuwa mujalladi uku. Read more: https://hausa.legit.ng/1267993-yanzu-yanzu-an-tsige-mataimakin-gwamnan-jihar-kogi-achuba.html
Legit Hausa
Ana saura wata daya gudanar da zaben jihar, an tsige
mataimakin gwamnan jihar Kogi, Simon Achuba. Majalisar dokokin jihar sun tsige
Mista Achuba ne a Lokoja, babbar birnin jihar, ranar Juma'a 18 ga Oktoba, 2019.
Shugaban masu rinjaye a majalisar ya bayyana hakan ne ga
manema labarai a zauren majalisar. Legit.ng ta kawo muku rahoton cewa Wani
kwamitin binciken a kan zargin da ake yiwa mataimakin gwamnan Kogi Simon
Achuba, wanda Barista John Baiyeshea ke jagoranta ya mika rahotonsa zuwa ga
Majalisar jihar.
Alkalin alkalan jihar Kogi, Jastis Nasir Ajanah shi ne ya
kafa wannan kwamitin. John kuma wanda shi ne shugaban kwamitin ya jagoranci
mika rahoton binciken zuwa ga Kakakin majalisar jihar a ranar Juma’a 18 ga
watan Oktoba, 2019. Kakakin majalisar, Kolawole Matthew ne ya karbi rahaton
daga hannun shugaban kwamitin a Majalisar jihar dake Lokoja.
Da yake magana bayan mika rahoton shugaban kwamitin ya ce
sun yi iya bakin kokarinsu na yin bincike na gaskiya. A cewar shugaban, John
Baiyeshea, a shirye kwamitinsu yake domin amsa duk wata tambaya da ta shafi
abinda rahoton nasu ya kunsa. Kuma ya kara da cewa rahoton ya kasu zuwa
mujalladi uku.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp