Legit Hausa
An fara kada kuri'u lami lafiya a rumfar zabe ta Dakta
Gukama mai lamba 007 da kuma rumfar zabe ta G/Kundi a mazabar Nasarawa da ke
karamar hukumar Birnin Kebbi amma mutane kalilan ne suka fito zaben.
A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na kasa (NAN), an fara
zaben karamar hukumar ta Birnin Kebbi tun karfe 7 na safiya bayan da aka kawo
kayayyakin zaben kuma jami'an zaben suka hallara. Jami'an Hukumar Zabe na Jihar
Kebbi (KEBSIEC) sun isa rumfunan zabe misalin karfe 7 na safe yayin da aka fara
jefa kuri'ar farko misalin karfe 8.43 na safe.
Daily Trust ta ruwaito cewa an fara zabe a mafi yawancin
rumfunan zabe misalin karfe 9 na safe inda jami'an 'yan sanda suka hallara don
tabbatar da tsaro. A mafi yawancin rumfunan zaben ana gudanar da zaben da
tantance masu zabe a lokaci guda ne sai dai mutanen da suka fito ba su da yawa.
An baza jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya da na Hukumar
tsaro ta NSCDC a rumfunan zaben duk da cewa al'umma ba su fito ba sosai.
Jami'in zabe na rumfar zabe ta G/Kundin Zouro, Abidina Abubakar ya ce ya isa
rumfar zaben karfe 7 na safe kuma suna tsamanin mutane za su fito domin su kada
kuri'unsu.
Wani jami'in zaben a
rumfar zaben Dakta Guluma, Faruku Muhammad ya ce dukkan kayayyakin zaben sun
iso kuma zaben na tafiya lami lafiya. Wani mai zabe, Abdulkarim Abubakar Atiku
Bagudu ya bayyana farin cikinsa kan yadda zaben ke tafiya lafiya kuma ya yi
addu'an Allah yasa a gama lafiya.
Shima gwamnan jihar, Atiku Bagudu ya ya yi murnar ganin
yadda mata suka fito kwansu da kwarkwata. Yayin kada kuri'arsa a rumfar zaben
Mai Alelu a mazabar Nasarawa a Birnin Kebbi, gwamnan ya yabawa KESIEC kan
kokarin da tayi na samar da isasun kayayyakin zabe. Ana gudanar da zabukan ne a
kananan hukumomi 21 na jihar.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp