Legit Hausa
Mohammed Babangida babban dan tsohon Shugaban Najeriya na
mulkin soja wato IBB ya ce, mahaifinsa ya fada masa cewa soke zaben 12 ga watan
Yuni, 1993 da yayi zai cigaba da bibiyarsa har tsawon rayuwarsa.
Soke wannan zaben ya jefa Najeriya da MKO Abiola cikin halin
rudani da takaici. Abiola a wancan lokacin shi ne ya lashe zaben da aka
gudanar.
Daga bisani bayan soke zaben aka kulle shi a gidan yari inda
ya mutu kafin a fito da shi. A cikin wata tattaunawa da jaridar The Sun babban
yaron Babangida ya bada labarin abinda ya faru a daren ranar da aka yi zaben.
Mohammed ya ce: “Muna zaune ne a falon fadar Shugaban kasa
wato Villa, sai mahaifinmu ya fito yake fada mana na soke zaben yau 12 ga watan
Yuni. Dukkaninmu sai muka dubi juna cikin mamaki, muka ce da shi, meyasa kayi
haka? “
Sai ya ce damu ku yara ne ba za ku fahimci dalilina na yin
hakan ba a yanzu. Sai muka ce ko da yake wannan abu ne wanda ya shafi mulkinka
da kuma gwamnatinka. Sai ya ce tabbas wannan abin zai cigaba da bibiyata har
tsawon rayuwata.”
Mohammed ya cigaba da cewa, tuni ‘yan Najeriya suka mance da
abinda ya faru bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya karrama Abiola da sanya
ranar 12 ga watan Yuni a matsayin ranar dimokuradiyyar kasar.
Haka zalika, soke wannan zaben yayi wa wasu ‘yan Kudu maso
yammaci amfani inda yake cewa wannan shi ne ribar soke zaben da mutane ba su
magana a kansa.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Tags:
LABARI