Rikicin Gabon da Amina Amal: Kotu ta sanya ranar da za ta yanke hukunci



Legit Hausa

Justis Obiora A. Egwuatu na babbar kotun Kano ya sanya ranar Laraba 23 ga watan Oktoba a matsayin ranar da kotun zata yanke hukunci bisa karar cin-zarafi da Amina Mohammed Amal ta shigar a kan cewa Hadiza Aliyu Gaon ta yi mata.

A ranar Laraban ne kotun za ta dubi wannan karar domin sauraron hujjoji daga bangaren Hadiza Gabon wadda ita ce ake kara. Haka kuma ana sa rana a ranar za a yita ta kare game da karar gaba dayanta.

Amal a cikin karar da ta shigar ta nemi kotu ta ba Gabon umarnin ba ta hakuri a gaban jama’a sannan kuma ta biyata tarar miliyan N50 saboda raunin da ta jimata a fuska. Sai dai kuma bangaren lauyoyin Gabon sam ba su aminta da wannan abubuwa da Amal ta bukata ba, inda suka cewa ai abin gaba dayansu ya faru ne a can wani wuri na daban inda bai cikin hurumin kotu.

Da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis 3 ga watan Oktoba jim kadan bayan fitowa daga farfajiyar kotun, jagoran lauyoyin Gabon, Barrister Sadiq Sabo Turawa ya ce: “Mun riga da mun mika duk wani bayani da kotun ke bukata na a dakatar da abinda Amal din ta nema.”

A dayen bangaren kuwa, lauyan Amal, Barrister Faruk Umar ya musanta bayanan takwaransa inda ya ce: “Muna jiran ranar cigaba da shari’a ne saboda mun san cewa hujjojinmu masu nagarta ne kwarai da gaske.
 

DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp

https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN