Legit Hausa
Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa sabbin
jiragen kasa 20 za su shigo Najeriya domin safarar jama'a a filin jirgin kasa
Abuja/Kaduna da Lagos/Ibadan nan da makonni shida masu zuwa. Amaechi ya bayyana
hakan ne a babban filin jirgin saman Nnamdi Azikwa Abuja yayinda ya dawo daga
kasar Sin.
Ya yi hira da manema labarai kan tafiyar da yayi zuwa Sin da
kuma abubuwan da ya je yi. Yace: "Abubuwa biyu suka kai mu, mafi muhimmanci
domin mu sayi sabbin jirage. Duk suna kasa. Za'a yi makonni shida kafin sun iso
Najeriya kuma za'a yi mako daya kafin tantancesu a tashar ruwa."
"Amma ga jiragen Legas, zai fi sauki, cikin kwana daya
ko biyu kadai za'a fara amfani da su. Amma jiragen Abuja sai an kwashe mako
daya kafin su iso nan." "Muna kyautata zaton samun sabbin jirage 20,
10 na Abuja-Kaduna, 10 na Legas -Ibadan a matsayin somintabi kawai, za'a karo
wasu kuma idan muka kammala layin dogon Legas-Ibadan."
Ministan ya bayyana cewa yayinda ganin sabbin jiragen a Sin,
ya gwadasu da kansa. Ya ce wadannan sabbin sun fi wadanda ake amfani da su
yanzu kyau a zamanance. He added that more trains were still being built for
Nigeria and the next batch would be delivered as soon as they are ready. Ya
kara da cewa akwai sabbin jiragen da ake kerawa Najeriya musamman kuma ana
kammala kerawan za'a turosu.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Tags:
LABARI