Legit Hausa
Gwamnatin tarayya na tsoron wani abinda kan iya zama matsala
ga tattalin arzikin Najeriya, a yinkurin da kungiyar ‘yan kwadago ke yin a
tafiya yajin aikin kasa gaba daya daga ranar 16 ga watan Oktoba. Jaridar
Tribune online ta ruwaito cewa, a jiya Juma’a 11 ga watan oktoba, gwamnatin
tarayya ta matso da ganawar da ta sanya a ranar Talata 15 ga watan Oktoba zuwa
ranar Litinin 14 ga watan don gudun shiga yajin aikin.
Duk da haka kungiyar kwadago na nan a kan bakarta, saboda a
daren ranar Juma’a ta sake fadin cewa maganar zuwa yajin aikin na daram dam. A
cigaba da shirin shiga wannan yajin aikin, kungiyar kwadago na sanar da
dukkanin ‘yan kwadagon cewa maganar yajin aiki fa babu fashi ranar Laraba za su
soma.
Tun daga ranar da maganar yajin aikin nan ta fito fili, hukumomin
gwamnati wadanda suka shafi minister kwadago, Chris Ngige, majalisar dattawa da
majalisar wakilai sun yita zama da kungiyar amma sai dai har yanzu a banza.
Abinda shugabannin kungiyar kwadagon ke korafi a kai shi ne,
ya za ayi gwamnatin tarayya ta sanya ranar Talata a matsayin ranar da za ayi
wannan zaman mai matukar muhimmanci duk da cewa sun san ranar Laraba kungiyar
za ta shiga yajin aiki.
Jaridar Tribune ta sanar da mu cewa zaman kungiyar kwadagon
da kwamitin kwadagon na majalisar dattawa bai tabuka wani abin a zo a gani ba,
saboda maganar yajin aiki fa tana nan daram.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Tags:
LABARI