Legit Hausa
Wani rahoto mai ban al'ajabi gami da takaici da muka yakito
daga jaridar Daily Nigerian ya bayyana cewa, wani bala'i ya auku a daren ranar
Lahadin da ta gabata cikin yankin Mabera dake birnin Shehu wato jihar Sakkwato
yayin da wasu dakarun sojin sama suka watsa al'ummar yankin tare da kashe
mutane biyu.
Mashaida sun bayyana cewa, wannan takaddama ta auku tun
yayin da tsokanar wasu matasan yankin ta fusata budurwar wani babban jami'i na
soja. Tsokanar matasan yankin ta sanya takaicin duniya ya ishi wannan budurwa
wadda hakan ya sanya ta labartawa saurayinta wanda ya kasance babban jami'in
tsaro irin abun da ke ci mata tuwo a kwarya.
Gogan naka bai yi wata-wata ba ya aike da mota guda cike da
dakaru domin daukar mataki a kan halin kunci da matasan yankin suka jefa
masoyiyarsa. Jaridar Daily Nigerian wadda ta ruwaito rahoton ta ce, sojoji sun
bi sahun daya daga cikin matasan wanda ya kasance dalibi, Abdulsalam Lawan,
bayan ya tsere har cikin wani gida da ya tare masa hanya.
Sojoji sun banka cikin wannan gida inda suka harbe matashin
da kuma wata uwar 'ya'ya bakwai da suka riska mai shekaru 40 a duniya, Maryam
Abdulrahman. Mashaidan wannan mugun ji da mugun gani sun zayyana cewa, wannan
ba shi ne karo na farko ba da sojoji suka saba cin zarafinsu.
"A daren jiya muna zaune dai a gaban wani teburin mai
shayi da misalin karfe 8.30 na dare, sojojin suka fara harbe-harbe cikin iska
inda kuma suka nemi wannan budurwa da ta nuna wadanda ke muzgunawa
rayuwarta".
"A yayin da ta gaza gano wadanda ke tsokanarta, sun
umarci dukkanin mazauna majalisar ta mai shayi da su yi tsallen kwado. Wadanda
kuma suka arce sojojin suka bi su da harbi". "Kimanin mutane biyar
sun raunata a sanadiyar harbi na harsashin bindiga a yayin da mutum biyu kuma
suka riga mu gidan gaskiya," inji wani mai bai wa manema labarai shaida,
Sani Mabera.
Ya zuwa yanzu an killace gawawwakin wadanda suka riga mu
gidan gaskiya a babban asbitin birnin Shehu domin gudanar da bincike. A yayin
da manema labarai suka rinka kwarara kira ta hanyar wayar tarho domin jin ta
bakin kakakin rundunar sojin saman Najeriya, Ibikunle Daramalo, bai amsa
kiraye-kirayen da aka rinka yi wa wayarsa ba ballanta sakonnin kar ta kwana da
aka aike masa.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp