Legit Hausa
Ma'aikatan gidan Zoo na jihar Kano sun bayyana cewa idan
hanyoyin da ake bi na damke Zakin da ya kwace ranar Asabar ya gagara, za'a
harbe dabban domin kare rayukan jama'a.
Daily Nigerian ta ruwaito. Mun kawo muku rahoton cewa Zakin
ya fasa cikin gidan Jimina kuma ya lashe daya kafin jami'an gidan suka turashi
cikin kejin akuyoyi kuma hallaka biyu.
Diraktan gidan Zoo na Kano, Saidu Gwadabe, ya bayyanawa
manema labarai a daren Lahadi cewa har yanzu ana cigaba da kokarin cewa na kama
Zakin da ransa. Gwadade yace kawo yanzu, Zakin ya kashe Jimina biyu da akuyoyi
da dama: "Zakin ya kwace gidan Jiminan kuma ya cinye biyu," a
cewarsa.
Ya kara da cewa a gayyato masana kiwon dabbobin gidan Zoo na
kasa sun dira Abuja domin bada gudunmuwarsa wajen kama dabban da ya kwace. Ya
ce har harbeshi da alluran kashe karfin jiki 10ml bayan ya shanye 1.5m kuma ba
tayi masa tasiri ba.
KALLI BIDIYO:
KALLI BIDIYO:
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp