Legit Hausa
Da yammacin Alhamis, Shugaba Muhammadu Buhari ya isa birnin
Makkah, domin gabatar da ibadar Umrah bayan kammala halartan taron sanya hannu
jari na tsawon kwana uku a birnin Riyadh. Shugaba Buhari ya dira filin jirgin
saman Sarki AbdulAziz ne misalin karfe 7:05 na Magariba.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ta bada rahoton cewa
shugaba Buhari ya samu kyayyakwar tarba daga wajen mataimakin gwamnan garin
Makkah, Bader bin Sultan bin AbdulAziz da wasu manyan jami'an gwamnatin kasar a
filin jirgin saman Sarki AbdulAziz.
Tuni shugaba Buhari da wadanda suka rakashi sun sanya izari
da rida'i. Daga cikin wadanda zasu gudanar da Umrah tare da shi sune gwamnan
jihar Katsina, Aminu Masari; gwamnan Kebbi, Atiku Bagudu da sauransu.
Kalli bidiyon:
President @MBuhari being received by the officials of Jeddah Province as he arrives Royal Terminals of King Abdul’aziz International Airport, Jeddah to perform Umrah (the Lesser Hajj) in the Holy City of Makkah. #PMBinKSA pic.twitter.com/SC2M677XJf— Bashir Ahmad (@BashirAhmaad) October 31, 2019
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp