Legit Hausa
Wani mai siyar da ruwa dan shekara 30 da aka kama yana
lalata yarinya yar shekara tara a Adamawa ya roki da ayi mai rangwame kan
hujjar cewa “bai kammala” ta’asar ba kafin aka kama shi.
Mai laifin, Mohammed Babangida, wanda hukumar tsaro na NSCDC
ta gurfanar a ranar Juma’a, 18 ga watan Oktoba, ya fada ma manema labarai cewa
shi sabon shiga ne a wajen aikata laifin, sannan cewa yayi danasanin abunda ya
aikata.
“Wannan shine karo na farko da na aikata hakan sannan banma
kammala ba lokacin da aka kwankwasa kofana, inda hakan ya tursasa ni dakatawa.
“Ina roko da a yafe mun a matsayina na magidanci dake da
yara. Ina zama a Bauchi; bana son wannan abun kunyan ya wargaza iyalina. Gaba
daya abun ya fara ne wasu yan kwanaki da suka gabata lokacin da yarinyar ta
roke ni N50 domin ta siya cincin, inda tayi ikirarin cewa tana jin yunwa, sai
na bata.
“Sai ya kara dawowa ta roke ni kudi a wata rana san na bata
N20; sai ta sake zuwa gidana na bata N50 sannan muka shiga daki,” inji
Babangida.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp