Legit Hausa
Rahoton da ke shigo mana da duminsa na nuna cewa shugaba
Muhammadu Buhari ya canza daya daga cikin ministocinsa, Barista Festus Keyamo.
Festus Keyamo wanda Buhari ya nada karamin ministan Neja Delta ya rasa
kujeransa amma an mayar da shi matsayin karamin ministan kwadago da daukan
aiki.
Legit.ng ta samu
wannan labari ne daga bakin Festus Keyamon da kansa da yammacin nan inda ya
bayyana wasikar a shafin ra'ayi da sada zumuntarsa ta Tuwita.
Yace: "Yanzunnan aka mayar da ni ma'aikatar kwadago
domin aiki da tsohon babban yayana, Chris Ngige."
Hakazalika, shugaba Buhari ya mayar da Tayo Alasoadura
ma'aikatar Neja Delta matsayin karamin minista. TheCable ta ruwaito cewa an
samu rikici tsakanin Festus Keyamo da Godswill Akpabio ne a ma'aikatar ta Neja
Delta.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN