Yadda wani saurayi ya yi wa matar mahaifinsa ciki a wata jihar arewa

A ko da yaushe, akan wayi gari da ji ko ganin wani abu ko lamari da ke iya daukan hankalin jama'a. Wannan labarin yadda wani matashi ya yi wa matar mahaifinsa ciki ne a garin Honk, da ke karamar hukumar mulki ta Awe a jihar Nassarawa.

Shi da kansa mahaifin yaron ne dan shekara 49 mai suna Musa Akur, ya kama dansa mai suna Audu tsirara turmi tabarya yana zina da matarsa mai suna Fatima yar shekara 33 a cikin dakin dansa Audu da misalin karfe 11:49 na dare.


Mujallar isyaku.com ya samo cewa mahaifiyar Audu ta rasu shekara 9 da suka gabata, sai mahaifinsa Musa ya auri Fatima, kuma yana gamsar da ita wajen kwanciyar aure.

Amma daga bisani sai ya auro wata mata ta 3, kuma bayanai sun ce daga lokacin ne ya daina saduwa da Fatima matarsa ta 2 a wajen kwanciyar aure. Dansa Audu yana sana'ar aski ne, wata rana ya dawo daga wajen sana'a kuma yana jin yunwa, sai ya je wajen uwargidan mahaifinsa domin ko zai sami tuwo ya ci amma ta ce da shi babu.

Daga bisani ya je wajen amaryar mahaifinsa watau matar mahaifinsa ta 3, ita ma ta ce da shi babu tuwo. Sai dai majiyarmu ta ce wadannan mata sun sha yi masa haka. Amma daga bisani Fatima watau matar mahaifinsa ta 2, ta kawo masa tuwo ya ci ya koshi. Daga bisani ta ci gaba da bashi labarin duniya a nishadance.


Audu ya ce " Bayan na gama cin abinci ne sai ta dauko labarin duniya , dama tana sanye da wani leshi da ya bayyana suran jikinta, daga bisani ta zo ta zauna kusa da ni ta sumbace ni, hankali na ya tashi, kaina ya girma, na rude da bege, ban san lokacin da na biye mata ba muka fara sumbata da rungumar juna".

Daga bisani ta jawo hannuna muka shiga daga cikin kuryar dakin, dama gidana ne, sai ta sa hannunta ta kwance wandon Jeans da nike sanye da shi, kuma ta zaro al'aura na ta fara tsotsawa, nan take na rude, na cire wandona muka fara lalata. Na sami fiye da minti 25 ina saduwa da ita, ita kuma tana nishin dadi da gamsuwa".

"Gaskiya na yi da na sani, yanzu asirinmu ya tonu, labari ya bazu ko'ina a Duniya, wannan abun kunya, amma babu yadda zan yi".

Sai dai majiyar mu ta ce tun kafin dubu ta cika, uwargidan Musa wanda ke sana'ar noma, ta ce tana zargin cewa Fatima tana nema da dansa Audu, amma Musa bai dauki maganar da muhimmanci ba, sai dai ya kirasu ya yi masu nasiha a kan illar irin wannan lamari idan ma suna aikatawa.

Wata rana Musa ya dawo daga tafiya da dare, sai uwargidansa ta ce su je gidan dansa wanda ke makwabta da gidan mahaifinsa, ta ce, matarsa Fatima tana tare da dansa Audu a gidansa. Sakamakon haka suka dunguma suka tafi gidan, amma abin da Musa ya gani shine babban abu mafi muni da ya taba gani a Duniya a cewarsa.

" Bayan mun isa gida ne tare da mata ta ta farko, sai muka tarar cewa basu rufe kofa ba, daga labule ke da wuya sai na gan dana Audu tsirara a kan matata Fatima ita ma tsirara suna lalata, ban san me nike yi ba kuma, na bude baki amma na kasa magana, uwargida na ce ta dinga kururuwa har jama'a suka taru a kan wannan abun kunya da dana da matata suka aikata. Wannan shi ne abu mafi muni da na taba gani a Duniya".

Wani abun mamaki shine yadda aka gano cewa Fatima tana dauke da cikin dan Musa watau Audu har tsawon wata 3, bayan ta shaida ma Audu cewa tana dauke da cikinsa, yaron ya nemi matar mahaifinsa Fatima ta zubar da cikin amma ta ki, a cewarta, ta dade tana neman juna biyu bata samu ba, yanzu kuma Allah ya bata, sakamakon haka ita wai ba zata zubar da cikin ba.


Fatima ta ce " Tun da muka yi aure, mijina Musa yana gamsar da ni wajen jima; kashi 100 bisa 100, amma bayan ya auro mata ta 3, sai ya daina tarawa da ni har tsawon shekara daya ko fiye, a duk lokacin da na bukace shi sai ya ce mani ko dai ya gaji ko ya kawo wani uzuri. Haka na yi ta hakuri da shi kafin in kasa jurewa bayan mun shaku da dansa Audu.".

" Dansa Audu ya fi mahaifinsa kwazo a kwanciya kuma yana gamsar da ni fiye da mahaifinsa da ya kyale ni fiye da shekara daya bai taba ni ba. Ai jiki ba katako bane.Ni ban aikata wani mugun abu ba, ciki ne dai na dauka ta hanyar saduwa da dansa ba wai wani jini ne daga waje ba. Ina nan daram a gidannan ba inda zan tafi".

Shi dai mahaifin Audu kuma mijin Fatima watau Musa, cewa ya yi " Ni dai ba zan ce masu uffan ba, zan sa masu ido kawai in gan yadda zasu yi da wannan ciki".

DAGA ISYAKU.COM

Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp

https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN